Skip to main content

Posts

Showing posts from September, 2020

MENENE ALJANNAR DUNIYA?!

SANIN SUNAYEN ALLAH DA SIFFOFINSA SUNE ALJANNAR DUNIYA ! Idan bawa yasan sunayen Allah da siffofinsa, kuma yayi ƙoƙarin roƙonsa dasu, yayi ƙoƙari wajen bautar ubangijinsa da ababen da suka ƙunsa, to tabbas wannan bawa ya sami  aljannar duniya wacce duk wanda bai shigeta ba tofa bashi ba shiga ta lahira . Domin kuwa, mafi girman rabauta da tsira acikin duniya shine bawa yasan ubangijinsa, kuma yasoshi, ya kusanceshi. Wannan shine farko abinda Allah-maɗaukakin sarki-ya ambata na daga ni'imomin da zai gabatarwa ma'abota aljannah. Allah maɗaukakin sarki yana cewa: “DA WAƊANDA SUKA RIGA, MADALLA DA WAƊANDA  SUKA RIGA, WAƊANNAN SUNE MAKUSANTA A CIKIN ALJANNA TA NI'IMAH” [Al-waƙi'ah/10-12] Sai Allah-maɗaukakin sarki ya fara ambaton kusancinsu kafin ya ambaci aljannah, kuma kafin ya ambaci dukkanin ababen da ya tanadar masu cikinta, na abinci ko abin sha ko mata da sauran ababen ni'ima.  Allah maɗaukakin sarki ya albarkacemu da ribatar ilimi mai amfani   Daga : Abul-Mustaph...

INDAI HAR ALLAH YA ƘADDARA..

  BABU MAI HANYAR TSEREWA ƘADDARA!   Allah maɗaukakin sarki shi yayi halitta kuma ya ƙaddari duk abinda zai wakana gareta akan tsarin da yaso, a cikin lokacin da yaso, babu kuma wanda ke da ikon samar da wanin tasgaro ko daƙile afkuwar abinda yayi nufin afkuwarsa.  Kenan, babu wajen tsira daga wani bala'i idan Allah ya ƙaddarasa ga bayinsa ! Don haka idan taka jarabtar ta iso gareka sai ka sanyawa zuciyarka natsuwa kuma kace : Allah ne ya ƙaddara kuma shi keda ikon aikata abinda yaso!  Ka tuna cewa lallai duk wanda yace shi me imani ne to ai dole yayi guzuri na juriya game da musibun da za'a jarabci imaninsa dasu. Don haka sai mu fuskanci jarabawarmu da karbabbiya kuma yardajjiyar fuskanta, domin duk wanda ya miƙa wuya ga Allah, Allah yana shiryatar da zuciyarsa zuwa ga rabauta. Allah maɗaukakin sarki ya yaye mana dukkanin ƙunci, kuma ya bamu ikon cinye kowace irin jarabawar da yake gwada imanin bayinsa da ita.  Daga : Abul-Mustapha Al-athary  September 5,...

KU ZURFAFA NAZARI DAI..

HAKAN BAYA TABA ZAMA HANYAR GYARA! Manzon Allah-tsira da aminci su ƙara tabbata a gareshi yana cewa: (( ﻣﻦ ﺃﺭﺍﺩ ﺃﻥ ﻳﻨﺼﺢ ﻟﺴﻠﻄﺎﻥ بأمر ﻓﻼ ﻳُﺒْﺪِ ﻟﻪ ﻋﻼﻧﻴﺔ، ﻭﻟﻜﻦ ﻟﻴﺄﺧﺬ ﺑﻴﺪﻩ فليخو به، فإن قبل منه فذاك، وإلّا كان قد أدّى الذي عليه له )) (( DUK WANDA YASO YAYI NASIHA GA SHUGABA TO KADA YA BAYYANAR DA NASIHARSA A FILI, SAIDAI YAYI RIƘO DA HANNUNSA YA KEBANCE DASHI, IDAN YA KARƁA DAGA GARESHI TO DAMA HAKA AKESO, AMMA IDAN BAI KARƁA BA TO SHI YA SAUKE HAƘƘIN DA YAKE KANSA )) Daga wannan hadeethi zamu iya fahimta cewa:  Baya halalta ga Malami, limami ko mai wa'azi ya haye kan minbarin juma'ah ko minbarin wa'azi yana tada jijiyoyin wuya wajen ambato aibi da laifukan shuwagabannin al'ummah! Babu maslaha cikin haka kuma babu hikima ko mithqala zarrah. Daga : Abul-Mustapha Al-athary May 13, 2016

IDAN ƁERA NADA SATA..

JAGORA DA WANDA AKE JAGORANTA   Allah madaukakin sarki ya raba ayyuka kuma yaba kowa nasa: 1- Shuwagabanni su riƙe nasu suyi ƙoƙarin saukewa, domin Allah zai tambayesu game da nauyin da ya dora masu.  2- Waɗanda ake shugabanta su riƙe nasu suyi ƙoƙarin saukewa, domin Allah zai tambayesu game da nauyin da ya ɗora masu.  Kada wani ya shiga aikin wani!  Duk wanda ya shiga aikin wani, ko yayi sakaci wajen zartar da nasa aikin, lallai ya saɓawa Allah maɗaukakin sarki. Shugabanci abune mai tsananin wahala, kuma lallai akwai hisabi tsakanin shuwagabanni da mabiya.  Duk wani shugaba wanda yayi amfani da jagorancinsa ko ƙarfin mulkinsa ya muzgunawa waɗanda yake jagoranta, lallai zai tarar da hukuncinsa a wajen ubangijinsa.  Tabbas haƙƙi ne ga shugaba ya tsarewa al'ummarsa ababe kamar haka:  (1)  Rayukansu    (2) Addininsu   (3) Dukiyoyinsu  (4) Hankulansu   (5) Mutuncinsu Da sauransu.   Haƙiƙa Allah maɗaukakin sarki...